18 Yuni 2025 - 05:13
Source: ABNA24
Iran Ta Kai Hari Akan Manyan Biranen Isra'ila + Bidiyoyi

Bayan wani sabon harin da Iran ta kai kan yankunan da aka mamaye, tashar 12 ta Isra'ila ta bayar da rahoton cewa, ana iya jin karar fashewar wasu abubuwa daga Ramat Hasharon da ke kusa da birnin Tel Aviv.

Hotuna da bidiyoyin da aka fitar daga garuruwan Tel Aviv, Herzliya, Ramat Hasharon da wasu yankuna da dama na nuni da cewa kusan makamai masu linzami 20 ne suka afkawa wurare daban-daban, inda suka yi barna da hasarar rayuka. Duk da cewa sama da sa'a guda kenan da harba makamin na Iran, har yanzu hayaki na tashi daga daya daga cikin gine-ginen da ke Tel Aviv.

Your Comment

You are replying to: .
captcha